1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

shirin bude taron ECOWAS akan Ivory Coast a Abuja

Zainab A MohammadOctober 5, 2006
https://p.dw.com/p/Btxq
Gamayyar Afrika
Gamayyar AfrikaHoto: AP

A gobe jumaa ne shugabannin kasashen yammacin Afrika ke gudanar da muhimmin taro adangane da farfado da yarjejeniyar zaman lafiya a Ivory Cost,kasar da aka dage gudanar da zaben shugaban kasa har sau biyu.

Taron wanda zai gudana a birnin Abujan tarayyar Nigeria,wanda kuma kungiyar ciniki na kasashen yammacin Afrika watau ECOWAS ta dauki nauyin gudanarwa,na fatan gano bakin zaren warware rikicin siyasa da kasar ta Ivory Coast mai arzikin Cocoa ke fama dasu.

An dai dora alhakin samar da sabuwar rana