1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shari´ar Saddam Hussain

November 28, 2005
https://p.dw.com/p/BvJ2

Nan gaba a yau ne, a kasar Iraki kotu za ta fara shari´ar tsofan shugaban kasa Saddam Hussain, tare da 7 daga wasu na hannun damar sa.

Kotu na tuhumar su, da kissan kiyasu a kan mutane 148 a garin Doujail,dake arewanci Bagadaza, tun shekara ta 1982.

Kotunan kasar Iraki, sun bayyana cewa wannan leffi,somin tabi ne daga dimbin leffikan da ake tuhumar tsofan shugaban kasar da aikatawa a zamanin mulkin sa.

Tun ranar 19 ga watan oktober da ta wuce a ka fara wannan shari´a amma a ka dage ta, dalili da rashin yan shaida.

A wannan karro, an tabbatar da cewa, za su hallarci kotun.

Saidai masu kulla da al´ammura a wannan kasa na bayyana cewa akwai alamun a yanzu ma a sake dage shari´ar don gudun karin yaduwar tashe tashen hankulla a yayin da ya rage kawanaki kalilan a gudanar da zaben yan majalisun dokoki.

A bangaren tashe tashen hankulla kam , su na ci gaba da wakana babu kakkabtawa.