1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shara ta kashe mutane takwas a Konakry

Gazali Abdou Tasawa
August 22, 2017

Mutane akalla takwas ne suka halaka a yayin da wasu da dama suka ji rauni a wata unguwar birnin Konakry babban birnin kasar Guinea a sakamakon zarftarewar wata dalar bola, biyo bayan wasu ruwan sama masu yawa.

https://p.dw.com/p/2if8X
Sierra Leone Freetown nach dem Erdrutsch
Hoto: Imago/Xinhua

Mutane akalla takwas ne suka halaka a yayin da wasu da dama suka ji rauni a wata unguwar 'yan rabbana ka wadata mu ta kewayen birnin Konakry babban birnin kasar Guine a sakamakon zarftarewar wata dalar bola, biyo bayan wasu ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka share mako daya ana zubawa a birnin. 

Kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya rawaito cewa da idanunsa ya ga lokacin da aka zakulo gawarwaki biyar da suka hada da na wasu kananan yara biyu daga karkashin bolar a unguwar yah ayyuhannasu ta Hamdallai.

Kwamishinan hukumar kula da harakokin tsaro a birnin na Konakry ya bayyana cewa dalar bolar ta rikito ne kan wasu gidaje uku, kuma yanzu haka jami'an ceto na can na kokarin zagulo wasu mutanen a karkashin gine-ginen da aka tabbatar na raye ya zuwa yanzu.