Schäuble na ganawa da takwarorinsa na jihohin tarayya.
November 16, 2006A yau ne ministan harkokin cikin gidan Jamus, Wolfgang Schäuble, ya buɗe wani taro a birnin Nürnberg, inda zai yi shawarwari da takwarorinsa na jihohin tarayya 16, a kan shirin da gwamnatin tarayya ke niyyar gabatarwa, na bai wa baƙi kusan dubu ɗari 2 da suka daɗe suna zaune a nan Jamus takardar izinin zama. Tuni dai, wasu daga cikin jihohin tarayyar sun bayyana adawarsu ga shirin, kuma sun lashi takobin yi masa babakere a majlisar mashawarta, saboda ganin da suke yi na cewa, hakan zai ƙara musu wani sabon nauyi ne a fannin kula da jin daɗin jama’a
Shirin dai, ya tanadi bai wa baƙin da suka shafe a ƙalla shekaru 8 suna zaune bisa ƙa’ida a nan ƙasar ne takardar izinin zama na dindindin, muddin sun nuna cewa za su iya kula da kansu, ba tare da dogaro kan hukumomin bai wa jama’a agaji ba.