A cikin shirin za ku ji 'yan rajin kafa yankin Biafra daga Najeriya na ci gaba da kokawa kan yadda dakarun tsaro a kasar ke gallaza musu a duk lokacin da suka fita zanga-zanga a daidai lokacin da rahoton kungiyar kare hakkin bil Adama ta Amnesty International ke nuni da cewa masu kayan sarki a kasar na cin zarafin kungiyyoyin farar hula da hana masu fafutika.