1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaman zulumi a Ghana yayin da ake jiran sakamakon zabe

December 8, 2016

Alamu na nuna za'a samu jinkiri wajen bayyana sakamakon zaben shugaban kasa dana 'yan majalisu a Ghana, bayan da hukumar zaben kasar, ta ce za ta sake nazarin alkaluman kidddiga, dangane da fargabar yiwuwar magudi.

https://p.dw.com/p/2TzEh

Hukumar zaben Ghana ta yi kiran kwantar da hankula yayin da ake jiran sakamako, tana mai cewa za ta bi diddigin dukkan sakamakon da aka kawo daga mazabu.Fafatawa a zaben dai tafi zafi ne tsakanin Shugaba John Mahama da kuma babban abokin hamaiyarsa Nana Akufo Ado.