Fiye da shekara guda mayakan Boko Haram sun sace Saratu da yaranta hudu Naomi, da Gochia, da Ramatu da kuma Ibrahim 'yan shekara 7 zuwa 14 daga kauyensu. Bayan wata takwas Saratu ta tsare.Yanzu kuma ta shiga neman yaran nata a sansanonin 'yan gudun hijira a Najeriya da Kamaru.