1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sakamakon zaɓen cika gurbi a Libanon

August 6, 2007
https://p.dw.com/p/BuEb

Ministan cikin gidan ƙasar Libanon, ya bada sakamakon zaɓen cika gurbin yan majalisar dokoki da aka gudanar jiya jiya a wasu yankuna guda 2 na ƙasar.

A Mertn an fafata tsakanin tsofan shugaban ƙasa Amine Gemayel, da kuma ɗan takara jam´iyun adawa Camille Khoury, mai goyan bayan madugun yan adawa Michel Aoun.

Sakamakon da a ka bayar ya nunar da cewa, tsofan shugaban ƙasar ya sha kayi, to saidai tuni, ya bayyana ƙinamin cewa da shi, wanda ya ce akwai maguɗi a cikin sa.

A yakin Beyruth dantakakara jam´iyun adawa, Momahed Amine Itani ya lashe zaɓen.

An gudanar da wannan zaɓɓuɓuka 2, domin cike gurbin yan majalisar dokoki 2, da su ka rasa rayuka a cikin wasu hare-haren ta´danci, wato Walid Eido da kuma Pierre Gemayel.