1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon shugaban Pilipin zai dawo da hukuncin kisa

Suleiman BabayoMay 16, 2016

Zababben shugaban Pilipin Rodrigo Duterte ya yi alkawarin zai dauki matakan da za su kawo karshen aikata laifuka ciki har da dawo da hukuncin kisa.

https://p.dw.com/p/1IoQs
Philippinen Präsidentschaftskandidat Rodrigo Duterte
Hoto: Imago/Kyodo News

Zababben shugaban kasar Pilipin Rodrigo Duterte ya ce sai sake dawo da hukuncin kisa kamar yadda ya yi alkawari lokacin yakin neman zabe.

Duterte ya sha alwashin kawo karshen miyagun laifuka a wannan kasa da ke yankin kudancin Asiya. Ya ce za a sake dawo da hukauncin kan laifuka kamar safarar miyagun kwayoyi, da fyade, da kisa, da kuma fashi da makami.

Rodrigo Duterte tsohon magajin garin Davao na kudancin kasar ta Pilipin ya lashe zaben makon jiya da gagarumin rinjaye, inda ranar 30 ga watan gobe na Yuni zai dauki madafun ikon kasar.