1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon salon siyasar Jam´iyyar ANC

Ibrahim SaniDecember 16, 2007
https://p.dw.com/p/CcKC

Jam´iyyar ANC a Afrika ta Kudu ta fara babban taron ƙolinta na wuni huɗu, da zai haifar da sabon shugaban Jam´iyyar na gaba. Ana dai wannan takara ne a tsakanin shugaba Thabo Mbeki da kuma tsohon mataimakinsa Jacob Zuma. Takarar shugabannin biyu, a yanzu hak ata haifar da darewar Jam´iyyar izuwa gida biyu. Duk wanda ya zamo sabon shugaban, bisa al´ada shi ya kann kasance shugaban ƙasar ta Africa ta Kudu. Duk da zarge-zargen cin hanci da rashawa daya dabaibaye tsohon shugaban, rahotanni sun ce Jacob Zuma ka iya samun nasarar lashe wannan zaɓe. Hakan dai nada nasaba ne da karɓuwarsa a tsakanin talakawa da kuma ma su fada aji a Jam´iyyar ta ANC.