Saɓin ƙasashe membobin Majalisar Ɗinkin Dunia
October 16, 2007Talla
Nan gaba a yau ne Majalisar Ɗinkin Dunia,zata zabi sabin ƙasashe 3 masu kujerun ƙayyaddaden lokaci a komitin Sulhu.
A na sa ran zaɓen Burkina Faso, Lybia, da Vietnam a matsayin sabin membobi na tsawan wa´adin shekara 2, wato 2008 da 2009.
Za su cenji ƙasashen Ghana, Congo, da Qatar a wannan kujeru.
Komitin Sulhu ya ƙunshi jimlar ƙasashe 15 membobi wanda su ka haɗa da 5 masu kujerun dindindin, wato Amrika France ,Britania, Russia da Sin.
A zaɓen sauran membobi n ko wace shekara 2, tsakanin ƙasashe 192 da Majalisar ta ƙunsa.
Saidai a halin da ake ciki, akwai mahaurta mai zafi, a game da wajibcin gudanar da kwaskawarima ga dokokin Majalisar Dinkin Dunia, tare da faɗaɗa komitin sulhu.