Rodolfo Adada shugaban tawagar hadin gwiwa ta MDD da UA a Darfur
May 8, 2007Talla
Majalisar Ɗinkin Dunia da ƙungiyar tarayya Afrika, sun zaɓi minsitan harakokin wajen ƙasar Kongo, Rodolfe Adada, a matsayin shugaban tawagar haɗin gwiwa ta ƙungiyoyin 2, a yankin Darfur na ƙasar Sudan.
Jmai´an na da yaunin jagorancin rundunar haɗin gwiwa da za ta gudanar da ayyukan tabatar da tsaro a wannan yanki da ke fama da tashe-tashen hankulla.
Wannan naɗi ya wakana a daidai lokacin da wakilin Majalisar Dinkin Dunia Jan Elliason, da na taraya Afrika Salim Ahmed Salim, su ka fara wani rangadi a yankin.