1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin 'yan aware a Kamaru na yin kamari

Abdullahi Tanko Bala
June 12, 2018

Wani rahoto da kungiyar kare hakkin bil Adama Amnesty International ta fitar, ta ce amfani da karfin soji da gwamnatin kamaru ke yi akan 'yan aware ya kara dagula lamura a kasar.

https://p.dw.com/p/2zO6Q
Kamerun Sprachenstreit um Englisch
Zanga zangar yan aware a KamaruHoto: Getty Images/AFP

Kungiyar kare hakkin bil Adama ta duniya Amnesty International ta ce matakin amfani da karfin soji da gwamnatin Kamaru ke yi a yankuna biyu masu amfani da turancin Ingilishi a kasar Kamaru inda yan aware ke neman ballewa domin kafa 'yantacciyar kasarsu ya kara tagula lamura.

A wani rahoto mai shafi 37 da kungiyar ta Amnesty International ta wallafa, ta ce ta tattara bayanai na cin zarafi da rusa gidaje da kamen babu gaira babu dalili da kuma azabtarwa da jami'an tsaron Kamaru suka rika yi akan jama'a tun daga karshen 2017.

Kungiyar ta ce irin wannan mataki na kuntatawa ba zai magance matsalar ba.

Kawo yanzu yankunan da ke magana da harshen Ingilishi a Kamaru na da yawan jama'a kimanin miliyan 22.