1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin SPLA da gwamnatin Sudan

Zainab MohammedNovember 19, 2007
https://p.dw.com/p/CJNN

Shugaban yankin kudancin Sudan Salva Kiir,ya zargi gwamnatin Khartum da shirin afkawa yankin da karfin soji.Bayan komawarsa gida domin fuskantar rikicin siyasa mafi daɗewa a Afrika da ƙasar sa ke fama dashi daga Amurka,Kiir ya fadawa Dubban gangamin waɗanda suka tarye shi cewar,bai komo gida domin ya shigar dasu faɗa ba,amma a shirye yake wajen ɗaukar matakai na kare kai.Wannan dai na mai zama sabon babi a sa in sa dake tsakanin jammiiyyarsa ta SPLM,da tsohuwar takwarar siyasar ta dake yankin arewaci.A watan daya gabata ne dai ministocin yankin kudancin Sudan ɗin suka fice daga gwamnatin shugaba Omar al-Bashir,adangane zarginsa da kin aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma a shekara ta 2005,wanda ya kawo karshen yakin sama da shekaru 20 a wannan kasa.