Rikicin siyasar kasar Kodivuwa ya ki ci ya ki cinyewa
October 19, 2006´Yan tawaye a Ivory Coast wato Kodivuwa sun yi fatali da kiran da kungiyar tarayyar Afirka AU ta yi na shugaba Laurent Gbagbo ya ci-gaba da jagorantar kasar da yaki ya daidaita har tsawon wata shekara guda. Shugabannin ´yan tawayen kungiyar New Forces sun yi suka ga karin wa´adin da cewa zai kawo cikas ga shirin samar da zaman lafiya. A na sa ran cewa a cikin mako mai zuwa za´a gabatarwa kwamitin sulhun MDD wannan shawara ta kungiyar AU don a amince da ita. AU ta kuma ba da shawarar fadada ikon FM Charles Konan Banny. A ranar 31 ga wannan wata aka shirya gudanar da zabe a kasar ta Kodivuwa, amma aka dage shi saboda ci-gaba da fada tsakanin kungiyoyin da ba sa ga maciji da juna a yankin dake hannun ´yan tawaye a arewacin kasar da wanda ke karkashin ikon gwamnati dake kudu.