Rikicin kasar Sri Lanka ya yi muni
June 17, 2006Talla
Wani kazamin fada ya barke tsakanin dakarun gwamnati da ´yan tawayen kungiyar Tamil Tigers a Sri Lanka. Wani kakakin rundunar sojin kasar ya ce jiragen saman yakin gwamnati da jiragen yaki na ruwa sun kai hare hare akan sansanonin ´yan Tamil Tigers bayan wani hari da ´yan tawayen suka kai kan wani caji ofis da kuma barikin sojin ruwa dake arewa maso yammacin kasar. Akalla mutane 24 ciki har da dakarun tsaro da kuma ´yan tawaye suka rasa ransu a gumurzun da aka gwabza a yankin. ´Yan tawayen sun kai harin ne don mayar da martani ga farmakin da sojoji suka shafe kwanaki biyu suna kaiwa akan garin Kilinochchi, cibiyar ´yan kungiyar Tamil Tigers. An kuma ba da rahoton fashewar wani abu mai karfin gaske a wannan yanki dake arewa da babban birnin kasar.