1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin kasar Nepal

April 8, 2006
https://p.dw.com/p/Bv2i

An kashe ´yan tawayen Mawo-ist guda 9 da kuma jami´an tsaro 3 a tashe tashen hankula da suka wakana cikin daren jiya a fadin kasar Nepal. Hakan dai ya zo ne a daidai lokacin da kasar ke fama da yajin aiki na gama gari da masu fafatukan neman mulkin demukiradiya suka shirya. Wata sanarwa da sojin kasar ta bayar ta ce dubban ´yan tawaye sun kai hare hare a lokaci daya akan sansanonin jami´an tsaro da kuma ofisoshin gwamnati a biranen Rupandehi da Kapilbastu. A kuma halin da ake ciki gwamnati ta kafa dokar hana fita da rana a birnin Kathmandu, inda ta yi gargadin cewa ´yan sanda zasu harbe duk wanda ya ki bin wannan doka. Mazaunma birnin sun ce an katse hanyoyin sadarwa na wayoyin salula da kuma intanat.