1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin Jamhuriyar Demokaradiyyar Kwango

Lateefa Mustapha Ja'afar
March 29, 2017

Rikicin siyasar Jamhuriyar Demokaradiyyar Kwango na ci gaba da yin kamari, bayan da masu ruwa da tsaki kan al'amuran da suka shafi al'umma da ke kokarin shawo kansa suka fara tsame hannunwansu.

https://p.dw.com/p/2aBxf
Shugaban Jamhuriyar Demokaradiyyar Kwango Joseph Kabila
Shugaban Jamhuriyar Demokaradiyyar Kwango Joseph KabilaHoto: picture alliance/AP Images/J. Bompengo

Guda daga cikin irin wadannan muhimman mutane da suka tsame hannunwa nasu dai, shi ne Archbishop Marcel Utembi wanda ke zaman mai shiga tsakani a rikicin da ya ce ya cire hannu a kan batun sulhun. Matakin na Archbishop Utembi dai baya rasa nasaba da abin da aka bayyana da rashin gaskiya daga bangaren manyan 'yan siyasar kasar. Rikicin na Kwango dai na kara ta'azzara bayan da jam'iyyun da ke cikin gwamnatin hadaka suka ki amincewa a nada Firaminstan rikon kwarya daga bangaren 'yan adawa, wanda zai rike ragamar mulkin kasar gabanin zabe. Tun dai da aka dage babban zaben kasar tare da kara wa'acdin mulkin Shugaba Joseph Kabila wanda wa'adin mulkin nasa ya cika ba tare da gudanar da zabe ba, kasar ta Kwango ta tsunduma cikin rikici.