Rasha ta yi kira ga Syria da ta ba da cikakken hadin kai a binciken kisan Hariri
November 26, 2005Ministan harkokin wajen Rasha Sergey Lavrov ya yi kira ga Syria da ta bawa jami´an MDD dake binciken kisan gillar da aka yiwa tsohon FM Lebanon Rafik Hariri cikakken hadin kai. A lokaci daya mista Lavrov ya ce bai kamata a sanya wata manufa ta siyasa a cikin binciken ba. A wata hira da yayi da takwaransa na Syria Farouk al-Sharaa ta wayar tarfo, Lavrov ya ce ya zama wajibi dukkan wadanda abin ya shafa ciki har da Syria da su ba jami´an binciken na MDD cikakken hadin kai. Yanzu haka dai Syria ta amince masu bincken na MDD karkashin jagorancin mai shigar da kara na Jamus Detlev Mehlis su yiwa jami´anta tambayoyi a game da kisan na Hariri a birnin Vienna. Syria ta saduda ne sakamakon matsin lamba da ta sha daga ketare. A kuma halin da ake ciki gwamnatin Lebanon ta yi lale maraba da wannan amincewa da Syria ta yi game da yi wa jami´an leken asirin ta tambayoyi a birnin na Vienna.