1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabuwar majalisar zartaswar Najeriya

Lateefa Mustapha Ja'afarNovember 11, 2015

Shugaba Muhammadu Buhari na Tarayyar Najeriya ya rantsar da majalisar zartaswarsa mai ministoci 36, abin da ya kawo karshen zaman jira na tsahon watanni.

https://p.dw.com/p/1H3zn
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu BuhariHoto: picture-alliance/AP Photo/C. Owen

Tun bayan da ya yi rantsuwar kama aiki a ranar 29 ga watan Mayun da ya gabata, Shugaba Buhari ya mayar da hankali ne wajen yaki da masu almundahana da kudaden al'umma da kuma yakar kungiyar Boko Haram. Birgediya Janar Muhammad Mansur Dan-Ali ne dai aka ba wa ministan tsaro yayin da aka Geoffrey Onyeama ya samu mukamin minstan harkokin kasashen ketare. An dai ba wa Babatunde Fashola tsohon gwamnan jihar Lagos mukamin minstan makamashi da ayyuka da gidaje, yayin da aka nada stohon gwamnan jihar Rivers Rotimi Amaechi a matsayin minsitan sufuri ita kuwa Kemi Adeosun ta samu mukamin ministar kudi. Fashola da Amaechi dai na zaman na kan gaba a jam'iyyarsu ta APC wajen tabbatar da ganin Buhari ya samu nasarar lashe mukamin shugabancin kasar. Ministocin na Buhari sun gaza na tsohon shugaban kasar Goodluck Jonathan, wanda ke da ministoci 42 a zamanin mulkinsa.