Ramaphosa: Za a binciki masu fariya da dukiya
February 21, 2018Talla
A cewar shugaban wannan mataki zai taimaka wa kasar ta Afirka ta Kudu a kokarin da ta sanya a gaba na yaki da cin hanci da rashawa.
Jam'iyyar ANC mai mulki dai ta bijiro da tsare-tsare na hanyoyin yaki da cin hanci inda a ka bukaci kwararru da hukumomi masu sa ido su shiga aiki ka'in da-na-in ta yadda za a zakulo mutanen da ke tafiyar da tsarin rayuwa da ta saba wa ka'ida ko ta almubazzaranci ta yadda za a yi bincike ko gurfanar da duk wadanda aka samu da aikata duk wani nau'i na cin hanci da rashawa.