1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Odinga: Babu raba madafun iko a Kenya

Yusuf Bala Nayaya
September 3, 2017

Dukkanin bangarorin biyu dai na masu mulki da bangaren adawa a siyasar kasar sun ja daga a shirin fita sake fafatawa a zabe.

https://p.dw.com/p/2jHd4
Kenia nach der Annulierung der Präsidentenwahl | Raila Odinga
Hoto: picture alliance/AP Photo/B. Curtis

Jagoran adawa a kasar KenyaRaila Odinga ya bayyana cewa ba zai shiga shirin raba madafun iko ba da gwamnatin da ke mulki a kasar yanzu. Odinga ya bayyana haka ne a wannan rana ta Lahadi kwanaki biyu bayan da kotun koli ta soke nasarar da Shugaba Uhuru Kenyatta ya yi a zaben watan Agusta ta kuma bada umarni na a sake zabe cikin kwanaki 60.

Dukkanin bangarorin biyu dai sun ja daga a shirin fita sake fafatawa a zabe inda za a sake gwarawa tsakanin Uhuru Kenyatta dan shekaru 55 da jagoran adawa Odinga dan shekaru 72, dukkanin bangarori biyun dai sun shiga yanayi na ci gaba da karta kasa.