1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

NPD za ta ci gaba da kasancewa halartatar jam'iyya a Jamus

January 17, 2017

Kotun tsarin mulki ta Jamus ta yi watsi da karan da aka shigar a gabanta na soke jam'iyyar NPD ta masu tsatsaura ra'ayi.

https://p.dw.com/p/2VvHi
Deutschland Karlsruhe Entscheidung des Bundesverfassungsgerichts zu NPD-Verbot
Hoto: Reuters/U. Deck

Dakin kolli na majalisar dokokin Jamus Bundesrat shi ne ya shigar da karan, kuma wannan shi ne karo na biyu tun daga shekara ta 2003 da ake gabatar da bukatar ta soke jam iyyar ta NPD.Sakamakon yadda ake yi ma ta kallon jam'iyyar da ke da manufofin 'yan Nazi, bayan wani kisan wariyar launin fata da wasu magoya bayan jami'yyar NSU suka yi a kan wasu bakin wacce ke kusa da jam'iyyar ta NPD.