1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar:Tsokacin jam'iyyun adawa

Mahaman Kanta AH
September 28, 2017

'Yan siyasar na Jamhuriyar Nijar na hadin gwiwar jam'iyyun adawa sun bayyana damuwarsu a game da halin da kasar ta samun kan ta a ciki na talauci da wahaloli da al'ummar ke fama da su.

https://p.dw.com/p/2kuq4
Hama Amadou, Parlamentspräsident in Niger
Hoto: DW/M. Kanta

Wannan ba shi ne karon farko ba da 'yan adawar na Jamhuriyar Nijar ke yin korafe-korafe na rashin halin ko in kula da gwamnatin ke nunawa a game da halin da al'ummar kasar ta samu kan ta a ciki na rashin ababen more rayuwa. Sannan kuma ga tsananin tsadar rayuwa da kuma talauci da ke adabar al'umma. Daya daga cikin shugabanin 'yan adawar na Njar dan majalisa Soumana Sanda ya ce abin takaici halin da al'ummar Nijar take a ciki a yanzu.