1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: Shekara daya bayan yamutsin dalibai

Abdoulaye Mamane Amadou AH
April 10, 2018

Dalibai a Nijar na zaman nuna juyayi na cikon zagayowar shekara guda da kisan da 'yan sanda suka hallaka wani dalibi Mala Bagalé Kelloumi a ranar 10 ga watan Afrilu a lokacin wani boren daliban.

https://p.dw.com/p/2vnsW
Niger Niamey Studentenproteste
Hoto: DW/Abdoulaye Mamane Amadou

Kusan dukkan dalibai sun dakatar da karatu a cikin dukkanin makarantu gwamnati da ma masu zaman kansu domin nuna alhini a zagayowar cikar shekara guda da kisan da 'yan sanda suka yi wa Mala Bagalé Kelloumi. A halin da ake ciki daliban na kokawa game da yadda har kawo yanzu gwamnatin ta Nijar ta gaza hukunta wadanda ke da hannu a kisan na daliban, duk kuwa da cewar gwamnatin ta girka wani kwamitin da ke gudanar da bincike.

Tun daga shekara bara daliban sun shiga cikin wani hali na yau karatu gobe yajin aiki sakamakon yadda suka ce gwamnatin ta yi yarjejeniya da su a kan bukatunsu amma kuma ta gaza cika alkawari.