1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: Issoufou ba zai yi tazarce ba

Abdoulaye Mamane Amadou | Lateefa Mustapha Ja'afar
April 3, 2017

A Jamhuriyar Nijer bangarori daban-daban na kasar na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu game da matsayin Shugaba Mahamadou Issoufou na cewar ba zai yi tazarce ba a karshen wa’adin mulkinsa.

https://p.dw.com/p/2aZP4
Shugaba Mahamadou Issoufou na Nijar
Shugaba Mahamadou Issoufou na NijarHoto: F. Batiche/AFP/Getty Images

Shugaba Mahamadou Issoufou wanda ya bayyana hakan ga manema labarai, ya kara da cewa yana fatan kasancewa shugaba na farko a tarihin kasar da zai damka mulki a hannun wani shugaban da 'yan Nijar za su zaba a shekara ta 2021 mai zuwa. Ya kara da cewa: "Ni dan siyasa ne tsantsa kuma ba ni da girman kan cewar ba wani  sai ni kadai ke iya jagorancin kasa, da akwai yan Nijer da dama da ke iya rike wannan matsayi, saboda haka fatana shi ne in shirya zabe mai tsabta tare da mika mika mulki ga hannun wani da al'ummar Nijar suka zaba, kuma ina jan hankulanku da cewar wannan zai zama karon farko a tarihin Nijar tun samun 'yancin kai."
 

Ko kalamansa sun karyata zargi?


Ba tun yau ba dai bangarori daban-daban na kasar ke ta hasashen take taken shugaban na makalewa a kan madafun iko duba da yanayi da halin tafiyar demokradiya a kasar mai cike da sarkakiya, sai dai wadanan kalamai na shugaban kasa tun daga yanzu sun haifar da da ra'ayoyi daban-daban kama daga fannin 'yan siyasa zuwa ga masu sharhi a fagen na Demokradiyya. Malam Sama'ila Amadou dan siyasa ne kuma shugaban jam'iyyar Awaiwaya na da ra'ayin cewa Shugaba Issoufou ya zuba ruwa ga wannan wuta. Wasu kungiyoyin fararen hula da ke rajin kare hakkin dimokradiyya kuwa na ganin in ba rami mai ya kawo batun ramin, ma'ana in dai ba yana da burin yin tazarcen ba mai ya kawo zancen tun yana da shekara guda a kan mulki? Sai dai ga wani mai sharhi a kan al'amurran yau da kullum kuma dan fafatukar kare hakkin dan Adam Alhaji Salissou Amadou na da ra'ayin cewa lokaci bai yi ba a yanzu, da ya kamata a soma wannan cece-kuce, yana mai cewa abin da ya kamata a sa a gaba a yanzu shi ne batun warware dinbin matsalolin da kasar ke ciki.

Yayin tattara sakamakon zaben da ya gabata a Jamhuriyar Nijar
Yayin tattara sakamakon zaben da ya gabata a Jamhuriyar NijarHoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo