1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nigeria na cigaba da binciken cutar masassarar tsuntsye

February 13, 2006
https://p.dw.com/p/Bv8D

Hukumomin lafiya a Nigeria na dakon sakamakon gwajin bincike akan wasu kananan yara biyu wanda ka iya zama karon farko na kamuwa da kwayar cutar murar tsuntsaye nauín H5N1 a tsakanin jinsin bil Adama a Afrika. Yaran wadanda ake zato sun kamu da cutar suna zaune ne a kusa da wata gonar kaji a jihar Kaduna dake arewacin Nigeriar. A kuma jihar Kano hukumomi sun fara wani gagarumin shirin kone kaji a matakin hana yaduwar cutar murar tsuntsayen. A nan Nahiyar Turai, kasar Slovania ta aike da samfurin kwayar cutar masassara tsuntsayen zuwa Britaniya domin gudanar da bincike mai zurfi. A kasashen Italiya da Greece da kuma Bulgaria nan ma, an sami bullar nauin kwayar cutar ta H5N1. A halin da ake ciki kungiyar tarayyar turai ta bukaci jamaá kada su firgita su kuma kwantar da hankalin su. Cutar masassarar tsuntsayen ta hallaka a kalla mutane 90 tun bayan da ta bulla a nahiyar Asia da kuma kasar Turkiya a shekarar 2003.