1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

NATO za ta kara yawan dakarunta a kasashen gabashin Turai

Mohammad Nasiru AwalOctober 8, 2015

Kungiyar ta kawancen tsaro za ta dauki wannan mataki ne don dakile barazanar da kawayenta na gabashin Turai ke fuskanta daga Rasha.

https://p.dw.com/p/1GkWf
NATO-Verteidigungsminister in Brüssel
Ministocin tsaron kasashen kungiyar NATO a BrusselsHoto: picture-alliance/AP Photo/V. Mayo

Kasashen Jamus da Amirka na son a girke karin dakarun kungiyar kawancen tsaro ta NATO cikin kasashe membobinta da ke gabashin Turai. Rahotanni sun ce ana iya tura daruruwan sojoji da za su ba da horo a kasashen Poland da Latviya da Estoniya da kuma Litawun wadanda ke fuskantar barazana daga Rasha dangane da rikicin kasar Ukraine.

A dangane da rikicin kasar Siriya kuwa inda yanzu haka Rasha take luguden wuta a kan mayakan IS, kungiyar ta NATO ta ce tana kuma tunanin karfafa yawan sojojinta a kasashe irinsu Turkiya. Babban sakataren kungiyar Jens Stoltenberg ya fadi hakan lokacin bude taron ministocin tsaro na kawance a birnin Brussels, inda ma ya kara da cewa.

"Muna fuskantar kalubale daga bangarori daban-daban. Ga rikice-rikice da rashin tsaro da kuma matsalar 'yan gudun hijira sakamakon rikicin a kasashen kudancinmu. NATO tana daukar matakan bai-daya na karfafa tsaronta mafi girma tun kawo karshen yakin cacar baka."