1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yakar talauci da rashin dai-daito

Lateefa Mustapha Ja'afarMarch 21, 2015

Sabon shugaban kasar Namibiya ya sha alwashin yaki da talauci da rashin dai-daito a tsakanin 'yan kasar.

https://p.dw.com/p/1Ev5J
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Lecocq

Sabon shugaban kasar Namibiya Hage Geingob ya yi rantsuwar kamun aiki watanni uku bayan da aka zabe shi a matsayin shugaban kasar. A yayin da ake rantsar da shi sabon shugaban mai kimanin shekaru 73 a duniya ya sha alwashin yin yaki da talauci da kuma rashin dai-daito a tsakanin al'ummar kasar dake da sama da mutane miliyan biyu. Geingob wanda ke zaman shugaban jami'iyyar South West Africa People's Organisation ya lashe zaben shugaban kasar da aka gudanar a watan Nuwambar bara da kaso 87 cikin dari tare da zamowa zababben shugaban kasar ta Namibiya na uku tun bayan da ta samu 'yancin kanta daga kasar Afirka ta Kudu a shekara ta 1990.