Najeriya:Sabbin alkaluma na hare-hare a garin Rann
January 21, 2017Talla
An kara samu bayanai na sabbin alkalluma na mutanen da suka rasa rayukansu a hare-haren da jiragen sama na yaki na rundunar sojojin Najeriya suka kai a makon jiya a garin Rann da ke a yankin arewa maso gabashin Najeriyar cikin Jihar Maiduguri bisa kuskure.Shugaban karamar hukumar Kala Balge inda aka kai harin Babagana Malarima ya ce mutane 236 suka mutu.Bayan da jiragen sama na yaki suka jefa bama-bamai biyu daya a kusa da wata rijiyar da ake gina wa 'yan gudun hijira,daya kuma a cikin wata unguwar da ke cike da jama'a makil.