1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Zawarawa sun kai kamfanin Shell kara

Yusuf Bala Nayaya
June 29, 2017

Cikin wadanda suka gabatar da karar dai akwai Esther Kiobel matar Barinem Kiobel, wanda aka ratayesu tare da marubucin nan dan fafutika Ken Saro-Wiwa a shekarar 1995.

https://p.dw.com/p/2fbe6
Ölplattform in Nigeria
Hoto: AP

Wasu mata hudu daga Kudancin Najeriya sun garzaya kotu a Holland don kalubalantar kamfanin Shell bisa zargin hannunsa a kisan da aka yi wa mazajensu a shekarun 1990, lokacin mulkin soja kamar yadda kungiyar kare hakkin bil Adam ta Amnesty International ta bayyana a wannan rana ta Alhamis.

Cikin wadanda suka gabatar da karar dai akwai Esther Kiobel matar Barinem Kiobel, wanda aka ratayesu tare da marubucin nan dan fafutika Ken Saro-Wiwa a shekarar 1995.

Wadannan mata dai da suka garzaya kotu da ke a birnin The Hague na neman abi hakkinsu kasancewar kamfanin na Shell na da hannu a wajen kame mazajensu, kafin daga bisani a kai ga kashesu a hannun gwamnatin soja, kisan da ya jawo tofin alatsine a duniya.