1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Yaki da cin hanci na fuskantar nakasu

Uwais Abubakar Idris
October 23, 2017

A Najeriya sake mayar da tsohon shugaban kwamitin binciken harkokin fansho Abdulrasheed Maina a bakin aiki duk da bincike da yake fuskanta na zargen salwantar da Naira bilyan 273 ya tayar da sabon cece-kuce.

https://p.dw.com/p/2mLjS
Nigeria Symbolbild Korruption
Kudin Tarayyar Najeriya na Naira.Hoto: picture-alliance/AP Photo/S. Alamba

Da alamu dai har yanzu ‘yan Najeriya basu manta da dauki ba dadin da aka tafka a kan tsohon shugaban kwamitin binciken hukumar 'yan fansho Abduraheed Maina, wanda a lokacin tsohuwar gwamnatin Shugaba Jonathan yake fuskantar zargin aikata ba daidai ba da kudadden ‘yan fansho da ta sanya hukumar EFCC bayyana nemansa ruwa a jallo amma kuma ya yi batan dabo. Sake maida shi a aikinsa  har ma da yi masa karin girma ya harzuka mutane da dama da jefa tababa a yaki da cin hanci da gwamnati ke yi.

Ta dai kai su ga wasan buya a tsakaninsa da 'yan majalisar dokokin Najeriya da suka bukaci gwamnati ta kore shi, kafin daga baya a gano cewa ita ce ma ke bashi kariya. Kungiyoyin farar hula da ke yaki da cin hanci da rashawa sun baiyana rashin jin dadi da rashin daukar mataki na hakika da ma kauda da kai a kan wadanda ake zargi da cin hanci da rashawa a karkashin gwamnatin ta Najeriyar. A yanzu dai kallo ya koma ga gwamnatin Najeriyar domin ganin matakin da za ta dauka a kan wannan batu.