Najeriya: An yi awon gaba da sandar majalisar dattawa
April 18, 2018Talla
Wani wanda al'amarin ya faru a kan idonsa ya shedawa kamfanin dillancin labaran Reuters cewa, ya na kallo mutanen uku suka shiga zauren majalisar suka kuma yi awon gaba da sandar a cikin dan kankanin lokaci. Mai magana da yawun majalisar Aliyu Sabi Abdullahi ya baiyana lamarin a matsayin laifin cin amanar kasa, Kawo yanzu ba a iya tantance mutanen ba da kuma dalilinsu na yin hakan. Bisa dokokin kasar, majalisar ba ta da hurumin aiwatar da doka ba tare da wannan sandar ba.