1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane tara sun mutu a bukukuwan Sallah a Ghana

Salissou BoukariJuly 7, 2016

Bukukuwan karamar Sallah sun haifar da rasuwar mutane tara sakamakon ture-turen da aka fuskanta a filin wasa na unguwar Asawase da ke birnin Kumasi na kasar Ghana.

https://p.dw.com/p/1JLGr
Bildergalerie Muslimisches Opferfest Eid al Adha 2012
Hoto: Reuters

Mutane tara ne suka mutu da yammacin ranar Laraba a wani filin taro na Asawase da ke karkashin majalisar karamar hukumar Asokore Mampong da ke birnin Kumasi na kasar Ghana, sakamakon ture-ture da aka fuskanta a lokacin da ake gudanar da shagulgulan karamar Sallah ta karshen Azumin watan Ramadan.

Da yake magana kan wannan hargitsi da ya faru, Nurudeen Hamidan da ke a matsayin shugaban karamar hukumar, ya tabbatar da mutuwar mutanen tara, maza shida da mata uku, dukkansu yara matasa. Ga al'ada dai matasa maza da mata dai ne ke haduwa a wannan fili a duk karshen watan Azumin Ramadan domin gudanar da shagulgulan Sallah.