1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane sun mutu a hare-haren Maiduguri

November 16, 2017

Hukumomi a Najeriya sun ce hare-haren da 'yan kunar bakin wake da aka kai birnin Maiduguri sun halaka mutane sama da goma yayin da wasu da dama kuma suka jikata.

https://p.dw.com/p/2nijH
Nigeria Selbstmordattentäter greifen Hilfs-Zentrum in Maiduguri an
Hoto: Getty Images/AFP/Stringer

Rahotanni daga Najeriya na cewa wasu jerin hare-haren da 'yan kunar bakin wake hudu suka kaddamar a birnin Maiduguri, sun halaka mutane akalla 18 yayin da wasu 29 suka jikata. Shaidu sun ce harin na yammacin ranar Laraba, ya kasance cikin mafiya muni da aka gani a birnin a bana.

Kakakin rundunar kakakin jami'an 'yan sanda a Borno, Victor Isukwu, ya ce maharan maza biyu mata biyu, sun afka wa wani waje ne mai yawan masu hada-hada a 'Muna Garage'. Harin na farko a cewar 'yan sandan an kaddamar da shi a wani wajen da mutane ke Salla, kuma maharan hudu sun mutu.

Hare-haren dai na zuwa ne yayin da rahotanni daga yankin Madagali dake arewacin jihar Adamawa ma ke tabbatar da wani harin na Boko Haram a yankin da yammacin na Laraba.