1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu ta saki shugaban IRA mai fafutuka a Murtaniya

Gazali Abdou TassawaMay 18, 2016

Kotun kolin Murtaniya ta bada umarnin sakin shugaban kungiyar IRA mai fafutkar yaki da ayyukan bauta a kasar da aka kama a watan Nuwambar shekara ta 2014.

https://p.dw.com/p/1Iq1d
Mauretanien Biram Dah Abeid Politiker
Shugaban kungiyar IRA ta Murtaniya da ke yaki da bauta Biram Ould Dah Ould AbeidHoto: Getty Images/AFP/Seyllou

Magoya bayan shugaban kungiyar ta IRA Biram Ould Dah Ould Abeid da mataimakinsa Brahim Ould Bilal sun barke da murna bayan daka bada umarnin sakinsu daga inda ake tsare da su. Da ya ke tsokaci kan sakin na mutanen biyu, lauyansu Brahim ould Ee Betty ya ce:

"Kotun koli ta soke matakin tsare su bisa hujjar cewa kotunan biyu da suka dauki matakin tsare 'yan fafutkar su biyu a baya, sun yi aiki ne da wani kudirin doka da bai dace ba."

Mauretanien Oberstes Gericht - Anhänger von Biram Ould Dah Ould Abeid
Hoto: DW/K. Diagana

A jawabinsa na farko jim kadan bayan fitowarsa daga kurkuku, Biram ya bayyana farin cikinsa da wannan saki da aka yi masa kuma ya kara da cewa mawuyacin halin da suka tsinci kansu shi da abokin gwagwarmayar tasa a cikin zaman kason bai sanya zuciyoyinsu suka karaya ba game da aniyarsu ta ci gaba da wannan kokawa tasu.

Guda daga cikin 'yan kungiyar da ke cikin wanda ke son cigaba da fadi tashin da suke yi Balla Toure ya ce:

Mauretanien - Anhänger von Biram Ould Dah Ould Abeid
Hoto: DW/K. Diagana

''Za mu ci gaba da kokawar yaki da bauta da ta kwace filayen noma da ake yi wa jama'a da duk wasu nau'o'i na bauta da na nuna banbancin launin fata dama na nuna wariya, domin mun yi imani cewa kokawar kwatar 'yanci ce kuma haka shi ne mafi alkhairi ga kasar Murtaniya"