1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mugabe ya fita bainar jama'a

Abdul-raheem Hassan
November 17, 2017

A karon farko shugaba Mugabe ya bayyana a bainar jama'a tun bayan da sojoji suka karbe iko. A cikin kayan bikin kammala karatun digiri, shugaban ya kasance cikin dalibai da ke bikin kammala karatun su.

https://p.dw.com/p/2nnwq
Simbabwe Robert Mugabe hält Rede an der Uni
Hoto: picture-alliance/AP Photo/B. Curtis

Dama dai a kowace shekara shugaba Mugabe na halartar bikin kamala karatun digiri na daliban jami'ar karatu daga gida, wato Open Univerty da ke kasar, sai dai a wannan karon 'yan kasar Zimbabuwe sun fidda tsammanin halartar shugaban ganin irin halin matsin lamba da ya tsinci kansa a ciki na daurin talala.

Sai dai har yanzu manyan sojojin kasar tare da wasu wakilan kasashe makota na ci gaba da tattauna batun yuwar yin murabus din shugaba Mugabe daga karagar mulki, yunkurin da ake hasashen zai seta al'amuran siyasar kasar da ke cikin rashin tabbas.

A ranar Laraba da ta gabata ne sojoji suka yi wa fadar shugaba Mugabe mai shekaru 93 dirar mikiya, tare da yi masa daurin talala na hanashi fita yayin da sojojin suka karbe ragamar kafar talabijin na kasa tare da mamaye babban birnin kasar Harare. Lamarin da 'yan kasar da sauran kasashen duniya ke wa kallaon tabbatuwar juyin mulki, amma sojojin suka musanta inda suka ce sun yi haka ne da nufin kakkabe 'yan siyasa da ke yi wa tattalin arzikin Zimbabuwe zagon naksa.