1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Moroko: Mutum 15 sun mutu a turmutsitsi

Ramatu Garba Baba
November 19, 2017

A kasar Moroko mutane akalla goma sha biyar ne suka mutu yayin da wasu biyar suka sami rauni a turmutsitsin da aka samu a lokacin da ake rabon agajin abinci.

https://p.dw.com/p/2ntju
Marokko König Mohammed VI
Hoto: Getty Images

Ma'aikatar harkokin wajen kasar ce ta sanar da faruwar lamarin inda ta ce an soma gudanar da bincike don sanin musababin aukuwar yamutsin a wannan yankin kasar da ke fama da tsananin talauci.Wani shedan gani da ido ya ce lamarin ya auku ne a yayin da daruruwan mata da suka hadu a harabar gidan wani attajiri da ya saba rabon kayan abinci ke rige-rigen karbar kayan abincin.