Ministan tattalin arziki na ƙasar Maroko na ziyarar Jamus don neman masu zuba jari a ƙasarsa.
November 17, 2006Yayin da ministan harkokin wajen Jamus, Frank-Walter Steinmeier, ke rangadi a ƙasashen Larabawa na arewacin Afirka, inda a yau ne ya da zango a ƙasar Maroko, ministan harkokin tattalin arziki na wannan ƙasa, Rachid Talbi El Alami, ya iso nan Jamus don neman masu zuba jari a ƙasarsa.. Da yake yi wa maneman labarai jawabi yau a birnin Berlin, minstan ya bayyana cewa, ƙasar Maroko na samu ci gaba sosai a fannin tattalin arzikinta. Ya ce a shekarar nan kawai ƙiyasi na nuna cewa, ƙasarsa za ta sami bunƙasar tattalin arziki na kashi 8 cikin ɗari. Amma duk da haka, Marokon na huskantar wasu mattsaloli. Kamar dai yadda ya bayyanar:-
„Muna ƙoƙarin kasancewa kan gaba a tserereniyar tattalin arzikin yankinmu. Kuma mu ne a kan gaban. Matsalar da muke huskanta a halin yanzu kawai ita ce rashin ƙwararrun ma’aikata. Sabili da haka, mun gabatar da wani sabon shiri na gaggawa, don mu iya horad da injiniyoyi dubu 10 a ko wace shekara.“