Ministan Kwadago na Britania ya yi murabus
November 2, 2005Ministan kwadago na kasar Britania David Blunkett yayi murabus daga mukamin sa a sahiyar yau laraba.
Masharahanta na nuni da cewa wannan murabus da wani na hannun damar Tony Blair ya yi zai kara saka Praministan a cikin wani saban yanayi da karya garfin gwiwa, bayan zargi da ya ke samu daga masu adawa da siyasar Britania a kasar Iraki.
A daya wajen kuma, kungiyar kare hakokin bani Adama ta Amnisty Internationl ta soki gwamnatinTony Blair da cin zarafin bani adama, ta hanyar sabin dokokin da ta bullo da su a yaki da ta´adanci.
Wannan dokoki inji kungiyar sun sabawa dokokin kariyar hakokin jama´a na kasa da kasa.
Britania, na daukar su domindadadawa Amurika, da ta shiga yaki ta ta´adanci tun bayan hare haren 11 ga watan Satumber na shekara ta 2001.