Sabbin matakan dakile barazanar ta'addanci a Jamus
August 11, 2016Talla
Ministan cikin gidan Jamus Thomas de Maizière ya kuduri aniyar daukar tsauraran matakan tsaro don dakile duk wata barazanar hare-haren ta'addanci a Jamus. Daga cikin matakan kamar yadda ministan ya sanar a birnin Berlin sun hada da tsananta sa ido kan baki da ke da alamun aikata laifuka da ake wa lakabi da masu hatsari ga kasa.
Ya ce: "Muna cikin wani lokaci mai hatsari. Barazanar ta'addanci ta kai kololuwa. Aikin ya yi wa 'yan sandar tarayya da na jihohi yawa. Gwamnatin tarayya da jihohi sun amince da daukar matakan ba sani ba sabo musamman wajen kai samame don riga-kafin duk wani hatsari ga al'umma."
A ranar Laraba jami'an tsaron Jamus sun kai samame a wasu wuraren kasuwanci da masallatai da ake zargi da tallafa wa 'yan tarzoma.