1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Merkel ta tattauna da DW kafin taron G7

Abdourahamane HassaneJune 6, 2015

Shugabar gwamnatin ta Jamus Angela Merkel ta ce za su tattauna kan kasuwanci da ɗumamayar yanayi da kiwon lafiya da maganar yaƙi da talauci da kuma samar da tsaro.

https://p.dw.com/p/1FcXF
Fernsehinterview der DW mit Bundeskanzlerin Merkel
Hoto: DW/C. Strack

Gabannin taron ƙasashe guda bakwai masu ƙarfin tattalin arzikin masana'antu a duniya wato G7 wanda za a soma a gobe Lahadi da Litinin a nan Jamus, Angela Merkel shugabar gwamnatin ta Jamus ta tattauna da DW a kan manufofin da taron ke shirin cimmawa, Wanda ya haɗa ƙasashen Faransa da Birtaniya da Japan da Canada da Italiya da Amirka da kuma Jamus ɗin mai masabkin baƙi,

Ta ce ''A wurina abIn da ke da mahimmanci a wannan ganawa da shugabannin ƙasashen guda bakwai shi ne mu canza yawu dangane da yadda za a iya shawo kan matsalolin da ke a gabanmu a cikin shekara mai zuwa, mu duba inda muke da saɓani ra'ayoyi da kuma inda bakinmu ya zo daya.''

An tsara taron zai taɓo batun kasuwanci da ɗumamayar yanayi da kiwon lafiya da maganar yaƙi da talauci da kuma samar da tsaro.