1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Merkel ta sanar da ministocinta na CDU

Abdullahi Tanko Bala
February 25, 2018

A yunkurinta na kafa sabuwar gwamnati, shugaba Angela Merkel ta nada sabbin jini da 'yan mazan jiya a mukaman ministoci daga jam'iyyarta ta CDU

https://p.dw.com/p/2tJlW
MASTER CINEMASCOPE +++ Kombo-Bild Politiker der CDU Ursula von der Leyen Jens Spahn Hermann Groehe Helge Braun Peter Altmaier Julia Kloeckner
Hoto: Getty Images/AFP/T. Schwarz/J. MacDougall/D. Roland/C. Bilan

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta nada wani matashin dan siyasa a jam'iyyarta wanda kuma ke yawan sukar shugabar inda ta nada shi mukamin minista a sabuwar gwamnati.

Matashin dan siyasar Jens Spahn mai shekaru 37 da haihuwa zai rike mukamin ministan lafiya.

Matakin dai ya nuna aniyar shugabar na shigar da masu sukar lamirinta a cikin gwamnati domin tafiya tare.

sauran nade naden sun hada da Julia Kloeckner wadda aka nada ministar ayyukan noma da kuma Anja Karliczek ministar Ilmi.