1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Merkel ta fara tattaunawa da jam'iyyu

Abdourahamane Hassane
January 7, 2018

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta ce suna fatan za a cimma yarjejeniyar kafa gwamnatin hadaka tare da jami'yyar 'yan gurguzu ta SPD.

https://p.dw.com/p/2qScu
Deutschland Sondierungsgespräche in Berlin Merkel und Schulz
Angela Merkel tare da shugaban jam'iyyar SPD Martin Schulz Hoto: Reuters/H. Hanschke

Angela merkel ta bayyana haka ne a taron tattaunawar da aka soma a birnin Berlin tsakanin jam'iyyun siyasar domin yin sulhu don girka sabuwar gwamnati. Sama da watanni uku ke nan da yin zaben 'yan majalisun dokokin a Jamus sai dai har yanzu babu gwamnati. Tun da farko a cikin watan Nuwamba da ya gabata Angela Merkel ta yi kokarin ganin sun cimma yarjejeniya da jam'iyyun siyasa na FDP da masu kare muhali na Greens hakan ya gaggara.