1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD:Ta ce ana cin zarafin bil Adama a Turkiyya

Abdourahamane Hassane
March 20, 2018

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ci gaba da tsawaita dokar ta baci a Turkiyya tun bayan juyin mulkin da ya ci tura a cikin watan Yuli na shekara ta 2016, ya sa gwamatin na ci gaba da galazawa al'umma.

https://p.dw.com/p/2udOy
Türkei Festnahme von Mitgliedern der Gülen Bewegung
Hoto: picture-alliance / ZUMAPRESS.com

A cikin wani rahoton da hukumar kare hakib bil Adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar, ta ce yanzu haka ana tsare da mutane kusan dubu 160 a gidajen kurkuku a tsawo watanni 18. Kana aka kori wasu ma'aikatan gwamnatin dubu 152 wadanda suka hada da malaman makaranta da alkalai da lauyoyi.