1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mbeki ya yabawa jamus

Zainab A MohammedJuly 9, 2006
https://p.dw.com/p/Bu6I

MBEKI

Shugaba Thabo Mbeki na kasar Afrika ta kudu yayi maraba da kokarin rundunar sojin Jamus wajen taimakawa samar da zaman lafiya a janhuriyar Democradiyyar Congo.Shugaban na Afrika ta kudu yace samarda zaman lafiya a Sudan da Congo ,nada matukar mihimmanci a zamantakewar nahiyar Afrika baki daya.Kimanin dakarun sojin Jamus 800 ne,zasu kasance a kasar janhuriyar democradiyya Congo,a bangaren kokarin da kasashen duniya keyi na samar da zaman lafiya da tsaro lokacin zaben kasar da zaa fara ranar 30 ga wannan wata.