Matsalolin aikin Hajji a Najeriya da Nijar
August 23, 2017Talla
Misali a Nijar mutane kamar dubu uku ne har yanzu suke jibge a filin jirgin samar birnin Yamai suna jiran gawon shannu, bayan sun riga sun biya kudadensu amma har yanzu jiragen da za su kwashe mutane sun gaggara. Yayin da a Najeriya ma a wasu Jihohin irin su Bauchi da Adamawa aka samu karancin jirangen saman domin kwashe maniyantan zuwa kasa mai tsarki. Hakan na zuwa ne daf da lokacin da ake shirin rufe karbar maniyanta a kasa mai tsarki.