1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mata uku sun kai hari a Maiduguri

Abdul-raheem Hassan
October 23, 2017

Mutane 13 sun mutu yayin wani harin kunar bakin wake da wasu 'yan mata uku suka kai a jihar Borno, harin da ya yi sanadiyar jikkata mutane 16.

https://p.dw.com/p/2mKRd
Nigeria Autobombe in Maiduguri 01.07.2014
Hoto: picture-alliance/AP Photo

'Yar kunar baken ta farko ta tarwatsa jigidar bam da ke jikinta ne da misalin 9:15 na daren ranar Lahadi a gaban wani gidan cin abainci. Sauran 'yan kunar bakin waken biyu, sun tashi bama-bamai da ke jikinsu ne jim kadan bayan tashin bam na farko wanda ya jikkata mutane da dama.

Jami'an soji da ke yunkurin fatattakan sauran 'yan kungiyar a Borno, sun ce wadannan jerin hare-hare sun faru ne sa'oi kalilan bayan samun wasu bayanan sirri na silalewar 'yan kungiyar Boko Haram a sassa daban-daban na jihar.

Babu dai wadanda suka dau alhakkin harin kawo yanzu, amma dai kungiyar Boko Haram ta sha ikirarin irin hare-hare makamantan wannan da ke kashe jami'an tsrao da fararen hula sama da 20,000 a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya.