1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Martanin ramuwar gayya a Afirika ta Kudu.

February 25, 2017

Kungiyoyin matasa a Najeriya sun kai hare-hare a kan kamfanoni 'yan Afirka ta Kudu a Najeriya a matsayin ramuwar gayya ga hare-haren da ake kai wa 'yan Najeriya da ke zaune a Afirka ta Kudun.

https://p.dw.com/p/2YDWp
Südafrika Straßenszene geschlossene Geschäfte in Joannesburg
Hoto: DW/M. Ayele

Hare-haren nuna kyama da suka faru a kasar Afirika ta Kudu a wannan karon sun yi wa jama'a da dama zafi a  Najeriya duk kuwa da matakan da mahukuntan kasar suka dauka na bayyana cewar suna tuntubar juna a mataki na diplomasiyya.Sanin cewa ba wannan ne karon farko da wannan ta taba faruwa. 

Matasan dai na masu nuna gazawar daukar matakai daga banagaren gwamnatin Najeriyar amma minsitar kasa a ma'aikatar kula da harkokin kasashen wajen Najeriyar Sanata Hon Khadija Bukar Abba Ibrahim ta ce suna daukan mataki a kan lamarin.A yayin da ‘yan sandan Najeriya suka gargadi duk masu kai hare-haren ramuwar a Najeriyar,matasan tuni suka yi kawanya a gaban ginin MTN da ma sauran kamfanonin da suke mallakar kasar Afirika ta Kudu a yanayi na jiran kadan,ya zuwa yanzu dai ana sa ido don ganin mataki na gaba da gwamnatin Najeriyar za ta dauka a kan wannan lamari.