Mali: Harin kwanton bauna ya hallaka sojoji uku
June 1, 2017Talla
Tun da wajejen karfe takwas da minti 40 ne na safe agogon kasar ta Mali, lamarin ya afku a sansanin dakarun Majalisar Dinkin Duniya na MINISMA da ke birnin Tombouctou a cewar mai magana da yawun dakarun sojojin kasar Faransa Kanal Patrik Steiger, wanda ya ce daya daga cikin sojoji takwas na Faransa da suka ji ciwo na cikin mawuyacin hali. Daga nata bangare rundunar sojojin kasar ta Mali cikin wata sanarwa, ta ce maharan sun halba wani babban makami ne a filin tashi da saukar jiragen sama na Tombouctou.